KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne na kai tsaye da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya a ranar Lahadi 13/09/2026

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Adeyemi Adeniyi
  • Abdourahamane Tchiani
  • Atiku Abubakar
  • NFF
  • Badriyyah Tijjani Kalarawi
  • Ranar Hausa: BBC
  • Danjuma Goje
  • Zainab
  • BBC
  • ABU
  • xxx
  • xxx
  • Khalifa Dokaji
  • Sheikh Jingir

Rahoto kai-tsaye

Isiyaku Muhammed

  1. 'Dabarar turai wajen taimakon Ukraine a yaƙi na haifar da sakamako mai kyau'

    UK

    Asalin hoton, Getty Images

    Mai bai wa gwamnatin Birtaniya shawara kan harkokin tsaro na ƙasa, Jonathan Powell, ya ce dabarar da Turai ke bi wajen goyon bayan Ukraine da kuma kakaba wa Rasha takunkumi na haifar da kyakkyawan sakamako.

    Da yake jawabi a wani taro da aka gudanar a birnin Kyiv, Powell ya ce ya zama wajibi kasashen Turai su kasance cikin shiri don fuskantar kowanne irin kalubale musamman a lokacin hunturun bana, domin ci gaba da matsa wa Moscow lamba.

    Ya ce duk da yiwuwar karancin iskar gas da ake sa ran za a fuskanta, bai kamata Turai ta sassauta takunkumin da ta kakaba wa Rasha ba.

    Jonathan Powell, ya kuma bayyana cewa Ukraine ta riga ta yi nasara a yakin, saboda har yanzu tana kan gaba a fafatawar da ake, sannan kuma Rasha ba za ta iya mamaye daukacin kasar ba. ends

  2. Ebola ta fara lafawa a DR Congo - Gwamnati

    Ebola

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kwango ta ce ta yi amannar cewa annobar Ebola da ake fama da ita a yanzu ta fara lafawa.

    Mai magana da yawun gwamnatin kasar ya bayyana a shafinsa na sada zumunta cewa an samu raguwar masu kamuwa da cutar tun daga tsakiyar watan Augustan da ya gabata.

    Wakilin BBC ya ce jami'ai sun ce cibiyoyin lafiya 10 daga cikin 61 na kasar ba su samu ko da mutum guda da ya kamu da cutar ba cikin makonni uku da suka gabata.

    Sai dai ya jaddada cewa har yanzu akwai bukatar a ci gaba da sanya ido tare da daukar matakan kariya domin kauce wa sake yaduwar cutar.

    Gwamnatin kasar ta ce an samu sama da mutum 7,000 da suka kamu da Ebola tun bayan barkewarta a watan Mayu. Hukumomi sun kuma ce kusan rabin wadanda suka kamu da cutar sun rasu.

  3. Yaƙin Yemen ya raba aƙalla mutum 76,000 da muhallansu - MDD

    Yemen

    Asalin hoton, Getty Images

    Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce aƙalla mutum 76,000 ne suka rasa matsugunansu a Yemen tun bayan da mayaƙan Houthi suka sanar da kafa shingen hana zirga-zirgar jiragen ruwa zuwa Saudiyya a watan Yuli.

    A cewar Majalisar Ɗinkin Duniya, adadin mutanen da aka raba da muhallansu ya ninka sau huɗu cikin makon da ya gabata, yayin da faɗa tsakanin dakarun gwamnati da Houthis masu ƙawance da Iran ke ƙara tsananta.

    A cikin wani rahoto kan “raba mutane da muhallansu da ke ƙara muni cikin gaggawa a Yemen”, Ƙungiyar Ƙasa da Ƙasa ta Kula da Hijira (IOM) ta yi gargadin cewa “sau da yawa iyalai baki ɗaya kan bar gidajensu da daddare, ba tare da wani wuri mai tsaro da za su fake ba.”

    IOM ta ce mafi yawan mutanen da aka raba da muhallansu na faruwa ne a yankunan gabar tekun yammacin ƙasar da kuma lardin Taiz.

    A cewar ƙungiyar, lardin Taiz ne ya fi fuskantar wannan matsala, inda kusan iyalai 8,300, waɗanda adadinsu ya kai kusan mutane 50,000, suka rasa matsugunansu a sassa daban-daban na lardin.

  4. Buɗewa

    Masu bibiyarmu a wannan shafi na kai tsaye daga BBC Hausa muna muku barka da safiyar yau Lahadi.

    Za ku iya ziyartar shafukanmu na sada zumunta domin kallon wasu hotuna da bidiyon hirarraki da muke wallafawa tare da yin tsokaci a kai.

    Da fatan ana hutun ƙarshen mako lafiya.