Dole ne kowa ya bi umarnin jagoran addininmu kan tattaunawa da Amurka - Iran

Asalin hoton, Getty Images
Shugaban Iran, Masoud Pezeshkian, ya jaddada cewa dole dukkan masu ruwa da tsaki su bi duk wata shawara da jagoran addinin ƙasar ya amince da ita wajen tattaunawa da Amurka, yana mai cewa wannan shi ne ginshiƙin yanke hukunci.
Ya bayyana cewa amincewar Majalisar Tsaron Ƙasa ita ce mafi aminci kuma duk abin da jagoran juyin juya hali ya sahale zshine ai zama wajibi ga kowa ya bi, ko da kuwa ra’ayinsa ya bambanta da na jagoranci.
A gefe guda kuma, kwamandan rundunar sararin samaniyar juyin juya halin Iran, Majid Mousavi, ya yi kira ga al’umma da su tsaya tsayin daka tare da goyon bayan jagororin ƙasa, ba tare da ja da baya ko ƙarin gaba ba.
Rahotanni sun kuma nuna cewa wasu ‘yan ra’ayin tsattsauran ra’ayi sun gudanar da zanga-zanga a Tehran, inda suka rika sukar manyan masu tattaunawa da Amurka, yayin da ake fargabar yarjejeniyar da ake shirin kulla tsakanin Iran da Amurka.
































