'Adadin mutanen da Isra'ila ta kashe a Lebanon sun kai 2,496'

Ma'aikatar lafiya ta Lebanon ta ce adadin mutanen da Isra'ila ta kashe tun daga ranar 2 ga watan Maris zuwa yau ya kai 2,496.
Cikin wata sanarwa da ta fitar a yau, ma'aikatar tace adadin waɗanda hare-haren Isra'ilan suka jikkata sun kai 7,725.
Isra'ila ta ƙi dakatawa da kai hare-hare Lebanon, duk da cewa an cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran, ko da yake tace yarjejeniyar ba ta haɗa da Hezbollah da take kaiwa hare-hare ba.
Ana ta yunkurin ƙara tattaunawa tsakanin Iran da Amurka wadda Pakistan ke shirin karɓar baƙunci a karo na biyu.













