Ministan harkokin wajen Iran ya tattauna da na Oman da Saudiyya kan mashigar Hormuz

Asalin hoton, Getty Images
Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araqchi, ya tattauna ta wayar tarho daban-daban da ministocin harkokin wajen Oman da Saudiyya kan halin da ake ciki a yankin da kuma hanyoyin rage tashin hankali.
Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta ce tattaunawar ta mayar da hankali ne kan halin da ake ciki a mashigar ruwan Hormuz da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.
A kwanan nan, Iran da Oman sun gudanar da tattaunawa mai ƙarfi ta kwanaki biyu, wadda ta zo daidai da dakatar da hare-haren sojin Amurka.
Jami’ai daga ɓangarorin biyu sun bayyana tattaunawar a matsayin mai amfani, sai dai Kazem Gharibabadi ya ce jiya Iran ba ta amince da tayin da Oman ta gabatar a yayin tattaunawar ba.
A gefe guda kuma, tattaunawar tsakanin Iran da Saudiyya ta zo ne a daidai lokacin da Saudiyya ta sanar a jiya cewa ta kakkaɓo wasu jirage marasa matuƙa da aka harba daga Iraq zuwa cikin ƙasarta.
A cikin ‘yan kwanakin nan, takun saƙa tsakanin Saudiyya da mayaƙan Houthi masu samun goyon bayan Iran ya sake tsananta, lamarin da ke ƙara tayar da hankali kan tsaron yankin Gabas ta Tsakiya.
























