KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 28/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Talata 28 ga watan Yulin 2026.

Taƙaitattu

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • xxx
  • Zahra Buhari
  • xxx
  • Nigeria
  • xxx
  • Davido
  • xxx
  • Zanga-zanga a aAfirka ta Kudu
  • xxx
  • Ummulkhairi Aliyu
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Arsenal

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Haruna Kakangi

  1. Ministan harkokin wajen Iran ya tattauna da na Oman da Saudiyya kan mashigar Hormuz

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araqchi, ya tattauna ta wayar tarho daban-daban da ministocin harkokin wajen Oman da Saudiyya kan halin da ake ciki a yankin da kuma hanyoyin rage tashin hankali.

    Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta ce tattaunawar ta mayar da hankali ne kan halin da ake ciki a mashigar ruwan Hormuz da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

    A kwanan nan, Iran da Oman sun gudanar da tattaunawa mai ƙarfi ta kwanaki biyu, wadda ta zo daidai da dakatar da hare-haren sojin Amurka.

    Jami’ai daga ɓangarorin biyu sun bayyana tattaunawar a matsayin mai amfani, sai dai Kazem Gharibabadi ya ce jiya Iran ba ta amince da tayin da Oman ta gabatar a yayin tattaunawar ba.

    A gefe guda kuma, tattaunawar tsakanin Iran da Saudiyya ta zo ne a daidai lokacin da Saudiyya ta sanar a jiya cewa ta kakkaɓo wasu jirage marasa matuƙa da aka harba daga Iraq zuwa cikin ƙasarta.

    A cikin ‘yan kwanakin nan, takun saƙa tsakanin Saudiyya da mayaƙan Houthi masu samun goyon bayan Iran ya sake tsananta, lamarin da ke ƙara tayar da hankali kan tsaron yankin Gabas ta Tsakiya.

  2. INEC ta ƙi amincewa da ƙara lokaci ga rijistar masu zaɓe

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya (INEC) ta ce ba za ta ƙara wa’adin rijistar masu zaɓe ba, duk da kiraye-kirayen da jam’iyyun adawa da ƙungiyoyin farar hula suka yi na a ƙara lokaci domin bai wa ƙarin mutane damar yin rajista.

    Mataimakin daraktan sashen wayar da kan masu zaɓe da hulɗa da jama’a na INEC, Wilfred Ifogah, ne ya bayyana hakan a wata hira da Gidan talabijin na Channels.

    Ya ce, “Dole ne mu kawo ƙarshen aikin rajistar a wannan lokaci. Don haka ga waɗanda ba su samu damar kammala rajistar ba, muna ba su haƙuri, amma a halin yanzu babu abin da za mu iya yi.”

    Tun da farko, INEC ta riga ta ƙara wa’adin rajistar da makonni biyu kafin daga bisani ta rufe a ranar Lahadi.

    A cewar Ifogah, ƙarin wa’adin da aka bayar tun farko ma ya jefa hukumar cikin ƙarin matsin lamba wajen kammala shirye-shiryen rijistar masu zaɓe kafin babban zaɓen shekara mai zuwa.

    Ya ƙara da cewa, “Bisa jadawalin ayyukanmu, muna buƙatar fiye da kwanaki 75 bayan an rufe rijistar domin tattarawa, tantancewa da shirya cikakken rijistar masu zaɓe kafin gudanar da zaɓe.”

  3. Ma’aikatan gwamnati fiye da 350 sun mutu a hare-haren Amurka - Iran

    Mai magana da yawun gwamnatin Iran, Fatemeh Mohajerani, ta ce fiye da ma’aikatan gwamnati 350 ne suka mutu yayin hare-haren da Amurka ta kai, lokacin da suke gudanar da ayyukansu na hidimtawa jama’a.

    Ta kuma bayyana cewa hare-haren sun lalata manyan kayayyakin more rayuwa da suka haɗa da gadoji 12.

    A cewarta, filin jirgin saman Bushehr ya lalace gaba ɗaya kuma zai buƙaci a sake gina shi, yayin da wani sabon jirgin fasinja da aka saya kwanan nan ya kasance cikin abubuwan da hare-haren suka shafa.

  4. An kashe ƴan Najeriya 98 a rikicin ƙyamar baƙi a Afrika ta Kudu

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Akalla ’yan Najeriya 98 ne suka mutu a hare-haren ƙyamar baƙi a Afirka ta Kudu tun daga shekarar 2022, a cewar gwamnatin Najeriya.

    Haka kuma, kusan mutum 1,500 aka tilasta musu tserewa daga ƙasar bayan an lalata gidajensu da dukiyoyinsu.

    A wata ganawa da aka yi a Abuja, ƙaramin ministan Harkokin Wajen Najeriya, Sola Enikanolaiye, ya zargi Afirka ta Kudu da gaza kare ’yan Najeriya da sauran baƙi a ƙasar.

    Ya ce da dama daga cikin waɗanda aka kashe ko suka jikkata mazauna ƙasar ne bisa ka'ida, yana mai allawadai da abin da ya kira ci gaba da hare-haren ƙyamar baƙi.

    Sai dai gwamnatin Afirka ta Kudu ta musanta goyon bayan ƙyamar baƙi, inda ministan hulɗar ƙasa da ƙasa, Lamola, ya ce an kama wasu da ake zargi da kai hare-haren kuma za a gurfanar da su a kotu.

    Ƙasashen biyu sun amince da ƙara tattaunawa kan batutuwan tsaro da hijira domin kare dangantakarsu.

  5. Oman ta gabatar wa Iran da sabon shawara kan yadda za a tafiyar da mashigar Hormuz

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito cewa ƙasar Oman ta gabatar wa Iran da wata sabuwar shawara kan kafa wata haɗaɗɗiyar hanyar gudanar da harkokin mashigar Hormuz tare da haɗin gwiwar ƙasashen yankin.

    Rahoton ya ce shawarar zai bai wa ƙasashen da za su shiga cikinsa damar ba da gudunmawa bisa raɗin kansu.

    Wani jami'in yankin da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa Reuters cewa shirin na Oman ya samu goyon bayan wasu ƙasashen yankin.

    Wannan na zuwa ne bayan da Iran ta sanar a ranar Litinin cewa ta yi watsi da wani shawara da Oman ta gabatar a baya na buɗe hanyar kudancin mashigar Hormuz har sai an cimma yarjejeniya.

    Sai dai duk da haka, ƙasashen biyu sun bayyana cewa tattaunawa mai ƙarfi da suka yi na tsawon kwanaki biyu a Tehran, a daidai lokacin da hare-haren Amurka suka tsaya, ta kasance mai amfani.

  6. Iraq ta musanta kai harin jirgi mara matuƙi zuwa Saudiyya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyar Dakarun Turjiyar Musulunci na Iraq ta musanta zargin da Saudiyya ta yi cewa Iraq ta harba jiragen yaƙi marasa matuƙa zuwa cikin ƙasar tana mai cewa ba ta da hannu a harin da aka kai kan cibiyoyin man fetur.

    Ƙungiyar, wadda ta ƙunshi ƙungiyoyin Shi'a masu goyon bayan Iran, ta ce hare-haren da ’yan tawayen Houthi na Yemen suka kai na da alaƙa da takunkumin da Saudiyya ke ƙaƙabawa Yemen.

    Haka kuma ta yi gargaɗi ga Riyadh kan ɗaukar matakin ramuwar gayya.

    A halin da ake ciki, firaministan Iraq, Ali Zaidi, ya ba da umarnin gudanar da bincike bayan Saudiyya ta ce ta kakkaɓo wasu jirage marasa matuƙa da aka harba daga Iraq.

    Gwamnatin Iraq ta kuma jaddada cewa ba za ta bari a yi amfani da ƙasarta wajen kai hare-hare kan maƙwabtan ƙasashe ba, yayin da Saudiyya ke zargin ƙungiyoyin mayaƙa masu goyon bayan Iran da kai harin.

  7. Tinubu ya ƙi ganawa da tawagar Afirka ta Kudu kan rikicin ƙyamar baƙi

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya ƙi ganawa da wata tawagar Afirka ta Kudu da Shugaba Cyril Ramaphosa ya aika domin tattauna rikicin kyamar baƙi da ke addabar ’yan Najeriya da sauran baƙi a ƙasar.

    Tawagar ƙarƙashin jagorancin ministan harkokin wajen Afirka ta Kudu, Ronald Lamola, ta gana da ƙaramin ministan harkokin wajen Najeriya, Sola Enikanolaiye, wanda ya ce hare-haren da ake kai wa baƙi bai kamata su lalata dangantakar ƙasashen biyu ba.

    Ya kuma bayyana cewa an kwashe kusan ’yan Najeriya 1,500 daga Afirka ta Kudu sakamakon rikicin.

    A nasa ɓangaren, Lamola ya sake jaddada cewa gwamnatin Afirka ta Kudu ba ta goyon bayan kyamar baƙi, yayin da Najeriya, Ghana, Kenya da Malawi ke ci gaba da kwashe wasu daga cikin ’yan ƙasarsu daga Afrika ta Kudu saboda hare-haren da ake kai wa baƙi tun watan Yuni.

  8. Netanyahu ya isa Washington domin ganawa da Trump

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya isa birnin Washington na Amurka domin ganawa da shugaban ƙasar Donald Trump.

    Ziyarar ta janyo hankalin jama’a a makon da ya gabata bayan maganganun ɗan takarar magajin garin New York, Zahran Mamdani, wanda ya bayyana yaƙin Gaza a matsayin “laifin yaƙi.”

    Ya kuma ce idan yana da ikon doka, zai iya bayar da umarnin kama Netanyahu idan ya je New York saboda zarge-zargen da ake yi masa a Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya (ICC).

    Sai dai washegari Mamdani ya janye kalamansa, yana mai cewa matsayinsa na magajin garin New York ba zai ba shi damar ɗaukar irin wannan mataki ba a hukumance.

    A wani ra'ayi da tsohon ministan harkokin wajen Iran Mohammad Javad Zarif ya wallafa a shafin Al Jazeera ranar Litinin, ya ce ziyarar Netanyahu zuwa Washington na da nufin rinjayar Trump kada ya kawo ƙarshen yaƙin da ake yi da Iran.

  9. Za mu biya Iran diyyar ɓarnar yaƙi da kuɗinta da ke hannunmu - Trump

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce gwamnatinsa za ta yi amfani da kuɗaɗen Iran da ke ƙarƙashin ikon Amurka wajen biyanta diyyar ɓarnar da yaƙin baya-bayan nan ya haddasa.

    Da yake magana da manema labarai a cikin jirgin shugaban ƙasa na Air Force One, Trump ya kuma yi watsi da rahotannin da ke nuna damuwa kan ƙarancin makamai a hannun Amurka bayan watanni ana kai hare-hare kan Iran.

    Ya ƙara da cewa tsohon shugaban ƙasar Joe Biden ya aika makamai masu yawa zuwa Ukraine, lamarin da ya sa Amurka ke ƙoƙarin sake cike ma'ajiyarta a yanzu.

    "Duk da haka, har yanzu muna da makamai masu yawa. A gaskiya muna da tarin makamai fiye da yadda za mu iya amfani da su," in ji Trump.

  10. An ji ƙarar fashewa da dama kusa da ofishin jakadancin Amurka a Iraq

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    An ji ƙarar fashe-fashe da dama a yankunan da ke kusa da ofishin jakadancin Amurka a birnin Erbil na yankin Kurdistan da ke arewacin Iraq, a cewar rahotanni daga kafafen yaɗa labarai na yankin.

    Tashar Al Jazeera ta ruwaito cewa an samu aƙalla fashewa bakwai a yankunan da ke kusa da ofishin jakadancin Amurka da wasu muhimman gine-ginen diflomasiyya a birnin.

    Sai dai kamfanin dillancin labaran Tasnim, wanda ake alaƙanta shi da dakarun kare juyin juya halin Iran, ya wallafa hotunan da ke nuna harin da aka kai kan sansanonin ƙungiyoyin Kurdawa masu adawa da gwamnatin Iran.

    Kamar yadda Al Jazeera ta ruwaito, Tasnim ma ta ce an samu fashewa bakwai, amma ta bayyana wuraren da hare-haren suka auku da Khalifan da Soran, waɗanda ke yankin Erbil a Iraq.

    Har zuwa yanzu, babu wani bayani a hukumance kan yawan asarar da aka yi ko irin ɓarnar da hare-haren suka haddasa.

  11. Iran ta ce duk wani yunƙurin toshe tasoshin ruwanta zai haifar da ƙazancewar yaƙi

    ....

    Asalin hoton, IRNA

    Iran ta gargaɗi cewa duk wani yunƙurin toshe tasoshin jiragen ruwanta da hana zirga-zirgar jiragen ruwanta ko na kasuwanci zai haifar da ƙazancewar yaƙin da ke tsakaninta da Amurka, tana mai cewa za ta mayar da martani ga duk wata barazana.

    A wata sanarwa da Hedikwatar rundunar sojin Iran, Khatam Al anbiya ta fitar, ta zargi Amurka da barazanar kai wa jiragen ruwa da tankokin man Iran hari kwanaki uku da suka gabata, tana mai cewa yin hakan tamkar faɗaɗa yaƙi ne a yankin.

    Gargaɗin na zuwa ne yayin da rikicin tsakanin ƙasashen biyu ke ƙara ƙamari, bayan tattaunawar diflomasiyya ta tsaya cik, yayin da shugaban Amurka, Donald Trump, ke ci gaba da yin barazanar ɗaukar matakin soja idan ba a samu gamsasshen sakamako ba.

  12. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Talata daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Aisha Babangida ce za ta kasance da ku a wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.