KAI TSAYE, Gasar Kofin Duniya da labaran wasannin BBC Hausa na ranakun 20 zuwa 26, Yuli, 2026
Wannan shafi ne da yake kawo muku labaran Gasar Kofin Duniya da aka kammala da kuma sauran labaran wasannin BBC Hausa na ranakun 20 zuwa 26 ga watan Yuli, 2026.
Arsenal ta ɗauki wani kwararren dan wasan gaban ƙasar Girka Christos Tzolis daga Club Brugge kan fan £34m.
Mai shekara 24 ya koma kungiyar da ta lashe Premier ne a abin da suka kira dogon kwantaragi.
Tzolis ya ci kwallo 43 a da bada 45 aka ci a wasa 108 da ya buga wa Clib Brugge.
Ya koma Arsenal ne saboda tafiyar Leadro Trossard zuwa Besiktas a farkon wannan watan.
Arsenal za ta so kare kambunta da ta ci bayan shekara 22 rabonta da shi.
Norway na shirin ɗaukaka ƙara kan jan katin Balogun
Asalin hoton, Getty Images
Hukumar kwallon ƙafa ta Norway na duba yiwuwar shigar da ƙara gaban kwamtin Fifa kan hukuncin janyewa dan wasan Amurka Folarin Balogun jan katin da aka ba shi a gasar kofin duniya.
Kamata ya yi ɗan wasan na Amurka ba zai buga wasan zagaye na 'yan 16 da ba da suka fafata da Belgium saboda katin da aka ba shi a wasan da suka doke Bosnia da ci 2-0.
Amma bayan shugaban ƙasar Amurka Donald Trump ya sa baki sai aka janye hukuncin dakatarwar da aka yi masa zuwa nan da wata 12.
Fifa ba ta bayar da wani dalili ba bayan ambato wata doka a kundinta da ta yarda a dakatar da hukunci kan ɗan wasa.
Daga baya Balogun ya buga wasan, kuma Belgium ta casa su da ci 4-1.
Cikin wata sanarwa da Hukumar NFF ta turawa BBC, shugaban Hukumar Lise Klaveness ya ce "za su dauki hukunci mai tsauri kan hakan" ba za su kyale ba.
Dama tun a baya NFF ɗin ta shigar da ƙara kan kyautar zaman lafiya ta Peace Prize da aka bai wa Trump tana ƙalubalantar rashin cancantarsa.
Saliba hutu ya ke buƙata ba tiyata ba - rahotanni
Asalin hoton, Getty Images
Rahotanni na cewa mahukunta Faransa da Arsenal sun cimma yarjejeniyar ba za a yi wa dan wasansu da ke buga baya aiki ba, saboda raunin da yake fama da shi.
Maimakon haka rahotannin sun ce 'hutu yake buƙata ba tiyata ba a bayansa'.
Saliba wanda ɗaya ne daga cikin jigo a tawagar Faransa da aka yi wa tsammanin taka rawar gani a kofin duniya amma Spain ta cinye ta a wasan kusa da na ƙarshe, kuma ta yi rashin nasara a hannun Ingila a neman na uku, ya buga wa ƙasarsa wasanni 7 a gasar.
Jigo ne shi a tawagar Arsenal da ta lashe gasar Premier a kakar da ta gaba, kuma ta je wasan ƙarshe a gasar Zakarun Nahiyar Turai ta Champions Lig.
Wasu masana dai na ganin yawan jinyar da matasan 'yan kwallo ke fama da ita, na da alaƙa da yawan wasannin da suke bugawa ƙungiyoyi da kasashensu, ba kuma sa samun cikakken hutun da ya kamata.
Villa ta karɓi Garnacho a matsayin aro daga Chelsea
Asalin hoton, Getty Images
Aston Villa ta amince da yarjejeniyar aro kan ɗan wasan gefe na Chelsea Alejandro Garnacho zuwa ƙarshen kakar 2026/27 tare da zaɓin saya.
Dan wasan mai shekara 22 ya kammala gwajin lafiyarsa a Birmingham a wani mataki na yarjejeniyar shekara huɗu idan Villa ta amince ta saye shi daga baya.
Ba dai a bayyana sharadin da sai an cika ba za a sayi ɗan wasan, amma za a bayyana ta ne da zarar an cika sharudan, kamar dai yawan wasannin da ɗan wasan na Argentina zai buga a kaka mai zuwa.
Chelsea ta yi amannar sharuɗan ba su da wuyar cikawa dan haka a ƙarshe za ta samu abin da take fata na darajar ɗan wasan da ta kai fan miliyan 43.
Barin Chelsea da ɗan wasan ya yi ya biyo bayan ɗan kar Morgan Rogers da aka yi kan kuɗi fan miliyan 117 a ranar Talata.
Guardiola na dab da zama kocin Italy
Asalin hoton, PA Media
Shugaban Hukumar Kwallon ƙafa ta Italiya Giovanni Malago ya ce sun tattauna da Pep Guadiola domin zama sabon kocin Italiya na gaba.
Pep da ya bayar Manchester City bayan kwashe shekaru 10 masu cike da nasara a Ingila, wanda cikinsu ya lashe Premier shida da FA uku da Kofin Lig biyar da kuma ChampionsLig ɗaya.
Italiya ba ta da kocin tun bayan da Gennaro Gattuso ya yi murabus a watan Afrilu saboda gaza samun tikitin gasar Kofin Duniya sama da sau ɗaya a jere.
Tun da fari Sky Italiya ce ta fara rawaito cewa wani abu na shirion faruwa tsakanin kocin mai shekara 55 da kuma Hukumar Kwallon Ƙafa ta Italiya FIGC.
A wata tattaunawa da ya yi da wata kafar labaran wasanni Malago ya tabbatar da alaƙar yana cewa "maganar kuɗi ce kawai ta yi saura tsakaninsu da Pep".
Hukumar kwallon ƙafa ta Italiya ta aike da wakilai da suka haɗa da mai koyar da dabarun wasannin ƙasar wanda tsohon dan wasanta ne Paolo Maldini da mai bashi shawara Leonardo sun je har Barcelona sun tattauna da Guardiola na tsawon kwanaki uku.
Newcastle ta amince ta biya £34m kan ɗan wasan Manaco Bamba
Asalin hoton, Getty Images
ƙungiyar kwallon kafa ta Newcastle ta amince da cinikin da ya kai £34m kan dan wasan tsakiya na Manaco Aladji Bamba.
Dan wasan na Faransa mai shekara 20 wanda ya fara bugawa ƙasar wasa a watan Agustan 2025, ya kamata ya isa Tyneside a ranar Alhamis ɗin yau domin yi masa gwajin lafiya ya kuma sanya hannu kan kwantaraginsa.
Newcastle ta sayar da Sandro Tonali ga Tottenham a watan jiya kuma ta shiga kasuwa domin samun wani matashin dan wasan ta dauka a karo na biyu, bayan ɗaukar Sean Steur dan shekara 18 daga Chelsea.
Wani wanda take shirin ɗauka shi ne Johan Manzambi daga Freigurg wanda ya zaɓi ya koma Aston Villa a makon jiya.
Ana binciken Inter Miami kan karya doka a cinikin Casemiro
Asalin hoton, Getty Images
Hukumar shirya gasar Major Lig Soccer ta Amurka ta ce tana bincike kan zargin karya dokar da ƙungiyar Inter Miami ta yi wajen ɗaukar dan wasan tsakiya na Brazil Casemiro.
A ranar Laraba ne Miami ta sanar da ɗaukar ɗan wasan mai shekara 34 da ya bar Manchester United a ƙarshen kakar nan.
Ya koma ƙungiyar ne bisa yarjejeniyar shekara guda amma akwai zaɓin tsawaita ta zuwa watan Yunin 2029.
Ba jimawa sai Hukumar MLS ta fitar da sanarwar tana 'duba zargin da ake na take doka a cinikin' kuma ana dora laifin ne kan ƙungiyar.
"Inter Miami na tara duk wasu bayanan da suka kamata masu alaƙa da cinikin domin kare kanta," a cewarsu.
Za a yi binciken ne kan damar da kungiyoyi ke da ita na ɗaukar ɗan wasa idan yana son ya je gasar.
Kazalika ƙungiyoyin gasar na da damar sanyi buƙatar daukar 'yan wasa biyar a lokacin guda, kuma za su iya cire wanda suke so ko su ƙara wanda suke so.
Ina son Mac Allister da Alisson su ci gaba da zama a Liverpool- Iraola
Asalin hoton, Getty Images
Kocin Liverpool Andoni Araola na son ɗan wasan tsakiya Alexis Mac Allister da mai tsaron ragar ƙungiyar Alisson su ci gaba da zama a ƙungiyar.
Dan wasan Argentina Mac Allister na da shekaru biyu da suka rage masa a ƙungiyar cikin shekaru biyar da ya sanya wa hannu lokacin da yazo a 2023.
Dan shekara 27 har yanzu bai fara magana kan sabunta kwantaraginsa ba, wanda hakan ya janyo jita-jita kan cewa zai bar Andfield a wannan kakar.
Iraola ya shaida wa manema labarai a Chicago cewa yana son fara wasannin share kaka a Amurka da waɗannan 'yan wasan nasa.
"Ina ganin Alexis na daya daga cikin 'yan wasa masu kyau na ƙungiyar nan cikin tsawon shekaru, kuma ya taka rawar gani a kofin duniya, dan haka ba wani abu ba ne wasu ƙungiyoyin su nemi manyan 'yan wasanmu," in ji kocin.
"Hakan na faruwa a kasuwar saye da sayerwar 'yan wasa.Kuma ni ina son ci gaba da aiki da yan wasana masu kyau. Kuma nan gaba zan ɗauki sabbin 'yan wasa."
Alisson na da shekara ɗaya da ta rage masa masa a Anfield kuma tuni Juventus ta nuna muradinta a kansa, Amma Araola a shirye yake ci gaba da aiki da golan mai shekara 33 a ƙungiyar.
Ina ganin ba sai an hukunta Leandro Paredes ba - Gavi
Asalin hoton, Getty Images
Dan wasan tsakiya na Spain Gavi ya ce shi bai amince a dakatar da dan wasan Argetina ba Leandro Paredes saboda fito na fiton da ya yi a filin wasa ba, bayan kammala wasan ƙarshe na Gasar Duniya.
Yan wasan Aregentina Parades da Molina da Almada da kuma mai taimakawa koci Roberto Ayala duka an gansu da hannu cikin rikicin lokacin da Spain ke murnar kammala gasar da ta ci 1-0.
An ga Parades ya shaƙi wuyan Eric ɗan wasan Spain da kuma kayar da Gavi yana yunkurin taushe shi yayin da shi ma Almada ya taimaka masa.
Parades bayan ya kayar da ɗan wasan na Barcelona ya nemi ya dake shi a fuska.
Tuni Fifa ta kafa kwamitin bincike kan lamarin, tare da alƙawarin tara mai tsoka kan duk wanda aka kama da laifi.
"Ban ga wani abun ɓacin rai ba, ba sai an dakatar da shi ba (Parades), kamar yadda Gavi ya shaida wa jaridar El Partidazo de COPE.
Sabbin fuskokin masu horarwar da za a gani a Nahiyar Turai
Bayan kammala gasar Kofin Duniya da aka yi a Amurka da Mexico da kuma Canada, rashin nasarar da wasu ƙasashe suka yi na neman zama sanadin kawo sauye-sauye a tawagoginsu.
'Yan wasa da dama sun ajiye takalmansu kazalika masu horaswa. Amma wannan maƙalar za ta yi duba kan wasu ƙasashe da ke neman kawo sauyi a fannin horarwarsu.
Faransa:
Tun gabanin rashin nasarar da ta yi a kofin duniya ake yaɗa jita-jitan cewa za a sauya mai horarsa da tawagarta.
An ta cewa tsohon kocinta Zinedine Zidane zai maye gurbin kocinta na yanzu Didier Deschamp.
Amma bayan rashin nasarar da ta yi a hannun Spain managa ta ƙara ƙarfi, manyan jaridu turai ciki har da Fabrizio Romano sun rawaito cewa Zidane zai jagoranci Faransa har zuwa June 2030.
Wannan na nufin zai jagoranci ƙasar zuwa manyan gasar da suka haɗa da Nations League 2027 Euros 2028 da kuma Kofin duniya 2030.
Zidane ya yi wasa da Deschamp a 1998, tawagar da suka ci kofin duniya bayan doke Brazil 3-0.
Asalin hoton, Getty Images
Jurgen Klopp:
Bai zo da mamaki ba jin cewa Jurgen Klopp zai zama kocin Jamus na gaba ba, saboda daɗewa da ya yi ba tare da wata ƙungiya da yake jagoranta ba.
Babban abin da ya tabbatar da burinsa na jan ragamar Jamus shi ne tattaunawar da aka yi tsakanin Hukumar kwallon Kafa ta Jamus da tsohon kocin tawagar Julian Negelsman ya ce sun cimma matsaya da hukumar kan ajiye aikinsa.
Hukumar ta tabbatar da cewa Jurgen Klopp zai jagoranci Jamus sai dai ba a bayyana tsayin lokacin ba da kuma lokacin da zai fara aiki.
Tun daga 2014 da Jamus ta ci Kofin Duniya a hannun Argentina, Jamus ba ta ƙara cin wasa ba a mataki na sili daya kwale.
Asalin hoton, Getty Images
Pep Guardiola:
Aikin gaban Pep Guardiola zai zama babba ne, domin zai farfaɗo da tawagar da ake ganin ta zama mushen gizaga.
Hukumar kwallon ƙafa ta ITaliya ta aike da wakilai da suka haɗa da mai koyar da dabarun wasannin ƙasar wanda tsohon dan wasanta ne Paolo Maldini da mai bashi shawara Leonardo sun je har Barcelona sun tattauna da Guardiola na tsawon kwanaki uku.
Pep wanda ya yi nasara a zamansa a spain lokacin da ya jagoranci Barcelona da zamansa a Jamus inda ya yi kocin Beyern Munich sai kuma inda da ya horas da Manchester City, watakila Itali ta zama inda zai yi kocin na gaba.
Zai iya zama koci na biyu dan wata ƙasar da zai jagoranci Italiya kuma na farko tun shekarun1960.
Tsofaffin 'yan wasan ƙasar irinsu Roberto Mancini da Andrea Pirlo suma sun nuna shaawarsu kan aikin.
Guardiola mai shekara 55, aikin ba zai bashi wuya ba saboda yana jin yaren Italiya sosai, lokacin da ya zauna a ƙasar tsakanin shekarar 2001 zuwa 2003.
Asalin hoton, Getty Images
Mark van Bommel:
Mark van Bommel tsohon dan wasan Barcelona kuma ɗan asalin Netherland rahotanni na cewa zai karbi aikin horas da Belgium na tsawon shekara biyu zuwa watan Yunin 2028.
Belgium ma kamar sauran ƙasashen da suka fuskanci koma baya a gasar kofin Duniya ta kai matakin wasan kusa da dab da naƙarshe a gasar inda gwarzuwar gasar Spain ta doke ta da ci biyu da ɗaya.
Rudi Garcia wanda tsohon dan wasan Faransa ne shi ne ya kai Belgium kofin duniya, kuma ya kabi aikin ne a 2025.
Ana sa ran Van Bommel zai jagoranci tawagar zuwa shekarar 2028, bayan gasar Euro.
Asalin hoton, Getty Images
Nijar da Mali da Burkina Faso na son karɓar baƙuncin Afcon
Asalin hoton, Getty Images
Ƙasashen Jamhuriyar Nijar da Mali da kuma Burkina Faso sun miƙa takardar haɗaka ta neman karɓar baƙuncin gasar ƙwallon ƙafa ta Afirka, Afcon a shekarar 2032.
Jami'an ƙasashen sun gabatar da takardar buƙatar ne ga shugaban hukumar ƙwallon ƙafa ta Afirka (CAF), Patrice Motsepe.
Shugabannin hukumomin kula da ƙwallon ƙafa na ƙasashen sun gana da Motsepe a birnin New York na Amurka a ranar Asabar, tare da Kanar Djibrilla Hima Hamidou, wakili a hukumar ƙwalllon ƙafa ta duniya FIFA, kuma ɗaya daga cikin manyan hukumar ƙwallon ƙafa ta Jamhuriyar Nijar.
A ranar Talata ne hukumar ƙwallon ƙafa ta Mali (FEMAFOOT) ta sanar da ganawar da aka yi, inda ta ce za a yi amfani da gasar wajen bunƙasa "haɗin kai tsakanin ƙasashen yankin da kuma haɓɓaka ƙwallon ƙafa a Afirka."
Miƙa takardar neman karɓar baƙuncin ta biyo bayan nuna sha'awar hakan da ƙasashen AES suka yi.
Hukumar ƙwallon ƙafa ta Mali ta ce za ta yi aiki tare da sauran ƙasashen biyu wajen yin "ingantaccen shirin karɓar gasar" wanda zai kawo sabon ci gaba a harkar ƙwallon ƙafa a nahiyar.
Har yanzu hukumar ƙwallon ƙafa ta Afirka ba ta riga ta zaɓi ƙasar da za ta karɓi baƙuncin gasar ta 2032 ba, gasar da ake yi duk bayan shekara biyu, tana tattara zaƙaƙuran masu taka leda na nahiyar.
A shekarun baya-bayan nan ne ƙasashen Mali da Nijar da Burkina Faso suka kafa ƙungiyar ƙasashen yankin Sahel ta AES bayan ficewa daga ƙungiyar haɓɓaka tattalin arziƙin ƙasashen yammacin Afirka (Ecowas), bayan jerin juyin mulki a ƙasashen.
AES ta ce manufarta ita ce bunƙasa haɗn kai tsakanin ƙasashen uku, musamman a ɓangaren tsaro da kasuwanci da kuma tattalin arziƙi.
Foden ya tsawaita kwantaraginsa a Man City
Asalin hoton, Getty Images
Dan wasan Manchester City Phil Foden ya sabunta kwantaraginsa a ƙungiyar na tsawon shekara huɗu zao ci gaba da zama a ƙungiyar har zuwa 2030.
Poden mai shekara 26 kwantaraginsa za ta ƙare ne a kaka mai zuwa, amma ya amince ya tsawaita ta ya yi aiki tare da sabon kocin ƙungiyar Enzo Maresca.
Dan wasan ya fara bugawa babbar tawagar Manchester City lokacin yana ɗan shekara 17 ƙarƙashin tsohon kocin ƙungiyar Pep Guardiola, daga nan ya buga wa City wasa 369 ya ci Premier shida da Champion Lig ɗaya da kuma FA biyu.
Kocin Ingila da ya jagorance ta zuwa kofin duniya Thomas Tuchel bai tafi da shi gasar ba, saboda rashin ƙoƙarinsa a kakar da aka ƙare, wadda ya fara wasa 23 a cikinta.
Forden ya ce "ya ƙagu ya fara wasa" ƙarƙashin Maresca wanda ya yi aiki tare da tsohon kocin ƙungiyar Guardiola.
Martinez na shirin taka leda a Argentina
Asalin hoton, Getty Images
Mai tsaron ragar Argentina Emi Martinez ya ce yana duba yiwuwar ko lokacin da zai hakura da buagawa ƙasarsa Argentina kwallo ya yi, bayan rashin nasarar da suka yi 1-0 a hannun Spain a wasan ƙarshe.
Dan wasan mai shekara 33 ya yi nasara a wasanni 67 da ya bugawa ƙarsarsa kuma ya buga duka wasannin da suka yi guda takwas a gasar kofin duniya ba tare da an sauya shi ba ko sau ɗaya, kuma kwallo takwas kawai aka ci shi.
Shi ne ya lashe kofin duniya a 2022, ya lashe kyautar golan da ya fi kowanne a gasar, kuma ya taka rawar a zo a gani a cikin gasar baki daya.
Shi ne golan Aston Villa tun 2020, kuma kwantaraginsa zai ƙare ne a 2029, ko da yake ana alaƙanta shi da tafiya Juventus a wannan kakar.
Lokacin saukar shugaban Fifa ya yi - in ji shugaban La Liga
Asalin hoton, Getty Images
Shugaban gasar La Liga ta Spain Javier Tebas ya yi kira ga shugaban hukumar kwallon kafa ta duniya Gianni Infantino ya sauka daga muƙamunsa.
Ya bayyana haka ne a wata tattaunawa da ya yi da wani gidan jari na La Gazzetta da ke Italiya, yana cewa Infantinno ' na neman lalata hukumar Fifa'.
Ya kuma soki yadda ake hutun shan ruwa ana tsaka da wasa a yayin gasar, da kuma wani hutu na gaira babu dalili da aka je a wasan ƙarshe lokacin da aka kammala hutun mintina 45 na farko, ka zalika ya yi batun janye jan katin da aka yi wa dan wasan Amurka Folarin Balogun da kuma shirin mayar da gasar kofin duniya ta ƙasashe 64.
Lokacin da aka tambaye shi ya kamata Infantino ya ajiye aiki sai ya ce " a ra'ayina eh, ya kamata, ina ganin lokacinsa ya yi."
Fifa ta fara bincike kan kan faɗan da aka yi bayan wasan karshe
Asalin hoton, Getty Images
Hukumar kwallon ƙafa ta duniya Fifa za ta fara bincike kan mummunar halayyar ta 'yan wasan Argentina suka nuna bayan kammala wasan ƙarshe na Kofin Duniya.
Fifa ta nemi kwamitin ladabtarwarta ya samar da wani kwamiti da zai bincike kan lamarin domin tabbatar da abin da ya faru a filin wasa na MetLife.
Duk ɗan wasa ko koci da aka samu da hannu cikin lamarin za a dakatar da shi, kuma za a ci tarar hukumar kwallon ƙafa ta Argentina.
Bayan rashin nasarar da ta yi a hanun Spain 1-0 a ranar Lahadi, wasu 'yan wasa da kuma mutanen tawagar kocin Argentina sun kama rikici da yan wasan Spain lokacin da suke murnar cin wasansu.
Nahuel Molina da Leandro Parades da Thiago Almada da mataimakin kocin Roberto Ayalla duka an gansu cikin rikicin.
Shugaban Uefa ya ƙauracewa wasan ƙarshe na Kofin Duniya don adawa da Fifa
Asalin hoton, Getty Images
Shugaban hukumar kwallon ƙafa ta Turai Aleksander Ceferin bai halarci wasan ƙarshe ba na kofin duniya da aka yi tsakanin Spain da Argentina domin nuna adawa da Fifa.
Ka zalika bai je wasan farko na gasar ba da aka yi tsakanin Mexico da Afrika ta Kudu a Mexico City, maimakon haka ya wuce New Jersey ne abinsa a ranar Lahadi, kuma hakan na faruwa ne sakamakon wasu hukunce hukunce da Fifar ta yi wanda yake adawa da su.
Uefa ta nuna rashin jin daɗinta a fili bayan janye wa dan wasan gaban Amurka Folarin Balogun dakatarwar jankatin da aka ba shi saboda sa bakin da Shugaban Amurka Donald Trump ya yi.
Wannan na daya daga cikin abubuwan da suka harzuƙa shugaban Uefa ya ƙi zuwa kallon wasan ƙarshe.
Uefa ta soki matakin da Fifa inda ta bayyana shi da abin takaici da ba a yi zato ba wanda babu dalilin yin shi.
Cin da aka yi mana akwai raɗaɗi in ji Messi
Asalin hoton, Getty Images
Dan wasan gaban Argentina kuma kyaftin ɗin tawagar Lionel Messi ya ce "akwai raɗaɗi" a rashin nasarar da suka yi kuma "zai ɗauki lokaci mai tsawo kan ya warke", yana magana ne kan 1-0 da Spain ta ci su a wasan ƙarshe na Kofin Duniya da aka kammala.
Dan wasan Spain na gaba Ferran Torres ne ya jefa kwallon a raga a lokacin da aka ƙara na minti 30 bayan cikar minti 90 da aka saba na wasa, wanda hakan ya kawo ƙarshen riƙe kofin da Argentina ke yi tun 2022.
Har da wannan Messi ya yi rashin nasara biyu a wasan ƙarshe da ya taɓa zuwa, har da na 2014 a hannun Jamus.
Dan shekara 39, da kamar wuaya ya halarci gasar ta 2030, ko da yake har yanzu bai bayyana ko zai hakura da bugawa ƙasarsa wasa ba.
Messi ya fashe da kuka bayan tashi daga wasan lokacin da aka sa masa sarƙar da ake bayarwa ga wadanda suka buga wasan ƙarshe.
"Ina taya Spain murna da lashe kofin nan da ta yi, ta zama gwarzuwar duniya", in ji Messi.
An yi ta sukar Fifa bisa zargin cewa tana dauke kai kan Argentina a gasar da aka kammala, sai dai daga Fifa har Argentina babu wanda ya ce uffan kan zarge-zargen.
Tsohon ɗan wasan Liverpool da Newcastle Keegan ya rasu
Asalin hoton, BBC Sport
Tsohon ɗan wasan Ingila kuma koci Kevin Keegan ya rasu yana da shekara 75.
Rasuwar tasa na zuwa ne bayan sanar da kamuwa da ya yi da ciwon Kansa da ta kai mataki na huɗu.
Daya daga cikin 'yan wasan Ingila da suka fi samun kyautuka a duniya, Keegan ya buga kwallo a Scunthorpe United, Liverpool, Hamburg, Southampton da kuma Newcastle lokacin da yake kan ganiyarsa.
Daga baya ya zama kocin Newcastle da Fulham da Ingila da kuma Manchester City.
A watan Yuni ne Keegan ya bayyana cewa yana fama da kansa a mataki na huɗu, wanda shi ne mataki mafi haɗari da ke nuna kansar ta bazu zuwa wasu sauran sassan jikinsa.
Colossal Cubarsi
Asalin hoton, Getty Images
Pau Cubarsí yana gaban duk wani dan wasa da ya halarci Kofin Duniya wajen:
Ya taɓa kwallo sau (139)
Ya ba da fassin ba tare da matsala ba sau (121)
Kashi (96%) na kwallo da ya ke bayarwa na zuwa daidai
Hana fassin kaiwa inda ake so (21)
Cire kwallo (6)
'Yan Spain na ci gaba da murna a Madrid
Daren jiya tamkar rana ya kasance ga magoya bayan kwallon ƙafa a Spain.
Ko mutum na kallon kwallo ko baya yi, dole yasa wani gagarumin lamari na faruwa a kasar.
Haka aka wayi gari, kuma ana ci gaba da jiran tawagar ƙasar ta dawo daga Amurka.