Ebola ta kashe sama da mutum 3,000 a Congo
Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo ta tabbatar da cewa cutar Ebola da ta barke a kasar har ta yi sanadin mutuwar fiye da mutum dubu uku, a yanzu ta bazu zuwa wani sabon yanki na kasar.
Gwamnan lardin South Ubangi da ke arewa maso yammacin kasar ya ce gwaje-gwaje sun tabbatar da nau'in cutar Ebolar na Bundibugyo, wanda ke haddasa barkewar cutar da ake fama da ita a yanzu.
Gwamnan ya bukaci mazauna yankin da su bi ka'idojin kariya da rigakafi, ciki har da yawaita wanke hannu da kuma kauce wa tarukan jama'a.
Wakilin BBC ya ce fargabar da ake yi lalle ita ce za ta iya yaduwa zuwa iyaka cikin wasu kasashen. Lardin South Ubangi na iyaka da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya da kuma Jamhuriyar Kongo-Brazzaville.